Hukumar kula da ma’aikata a garin Buea da ke yankin kudu maso yamma ta tilasta wa ma’aikatan gwamnati su ringa halartar gasar cin kofin kasashen Afirka.
Hakan dai ya biyo bayan umarnin da gwamnan yankin ya bayar, kamar yadda magajin garin ya nuna cewa halartar filin wasan wajibi ne ga kowa.
Matakin ya zo ne bayan an buga wasanni da dama a garin Limbe inda mutane kadan ne suka shiga filin wasan.
Mazauna yankin ba Buea da dama na fargabar samun arangama tsakanin ƴan a-ware da sojoji.
‘Yan a-waren waɗanda suka ƙaddamar da yaƙi da gwamnati shekara biyar da ta gabata sun yi barazanar kawo tsaiko a wasannin, amma gwamnati ta tabbatar da samar da tsare.
Birane da dama sun samar da motocin bas-bas da ƙananan motoci don ba wa mutane da yawa damar halartar wasannin.
A ranar Asabar gwamnatin ƙasar ta Kamaru ta rage sa’o’in aiki.
Ma’aikata a ofisoshin gwamnati da ma’aikatu sun fara tashi daga aiki daga ƙarfe biyu na rana daga ranar Litinin, yayin da ake tashi daga makarantu da ƙarfe daya.
I have been browsing online greater than 3 hours as of late, but I never discovered any fascinating article like yours.
It’s pretty worth sufficient for me. In my view, if
all site owners and bloggers made good content material as you did,
the internet shall be much more helpful than ever
before.
Hey very nice blog!
Greetings from Idaho! I’m bored to death at work so I decided to browse your blog on my iphone during lunch break.
I enjoy the information you present here and can’t wait to
take a look when I get home. I’m shocked at
how quick your blog loaded on my mobile ..
I’m not even using WIFI, just 3G .. Anyhow, superb site!