In dai Gwamna Matawalle Zai Sauka daga Mukaminsa, Nima a Shirye Nake na Sauka – Mataimaki Gwamnan Zamfara

Date:

Daga Umar Sani K/Naisa
Mataimakin Gwamnan jihar Zamfara Barr. Mahdi Aliyu Muhd Gusau ya mayar da martani ga Gwamnan zamfara Bello Matawalle, kan ikirarin da yayi na sauka daga kan kujerar Gwamnan jihar.
Barrister Mahdi Aliyu Mohammed Gusau ya ce a shirye yake ya bada takardar barin aikin a matsayinsa na mataimakin gwamnan jahar Zamfara muddin Gwamna Matawalle zai rubuta tashi takardar ta barin mukammin sa na Gwamna kamar yadda yayi ikararri ya yin wata hira da yayi da manema labarai a gidan Gwamnanitin jihar.
 A wancan lokacin Gwamnan yayi rantsuwa da Allah cewa ba don sanin da yayi cewa Mataimakin Mahdi Ali Gusau ne zai hau kujerar Gwamna ba bayan shi Matawallen ya sauka, da tuni ya sauka daga kujerar ta Gwamnan.
Da yake mayar da martani ga Gwamnan, Mataimakin Gwamnan yayi Allah waddai da wannan magana wadda ya kira ta tamkar soki burutsu . Ya zargi Matawalle da laifin wasa da hankalin mutannen jihar zamfara.
Cikin wata sanarwa da Sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na Jihar Abba Bello ya Sanyawa hannu kuma aka aikowa kadaura24 yace mataimakin Gwamnan ya kara jaddada cewa a shirye yake ya rubuta takardar barin aikin a duk ranar da shi Gwamnan zai rubuta tashi.
Ya kara da cewa wannan kudurri da matamaikin Gwamnan yayi na barin aiki tare da shi da gwamna Matawalle yana daga cikin sadaurkawar da za su yi don ganin an ceto jahar Zamfara daga mummunan halin da ta samu kanta. Ya kuma kara da ba Gwamna Matawalle shawara daya mayar da hankali wajen shirrin yadda zai tafiyar da rayuwar shi bayan ya sauka daga mulki wanda ga dukkan alamu ya kusa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...