Twitter sun ce sun ji dadin dawo wa Nigeria

Date:

Dandalin sada zumunta na Twitter ya bayyana jin daɗinsa game da matakin gwamnatin Najeriya na dawo da ayyukan shafin a ƙasar bayan wata bakwai.

“Mun ji daɗi ganin cewa mutanen Najeriya na iya amfani da Twitter,” a cewar kamfanin.

“Muna matuƙar son yin aiki a Najeriya, inda ake amfani da Twitter don kasuwanci da sadar da al’adu da kuma tattaunawa,” in ji Twitter cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinnsa na dandalin ranar Alhamis.

A ranar Laraba ne wata sanarwa daga fadar gwamnati ta ce Shugaba Buhari ya amince a cire haramcin amfani da Twitter daga 12:00 na daren Laraba.

Gwamnati ta rufe shafin ne a watan Yunin 2021 bayan ya goge wani saƙo na Buhari kan ‘yan bindigar da ke tayar da hankali a yankin kudu maso gabashin ƙasar, tana mai zargin kamfanin da yaɗa labaran “raba kan ƙasa”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...