Yajin Aikin Yan adaidaita: Yan Sanda Sun Kama Mutane 40 a Kano

Date:

Rundunar ‘yan sanda ta kasa reshen jihar Kano ta ce ta kama kimanin mutum 40 bisa zargin afka wa wasu masu sana’ar babur mai kafa uku, saboda kin shiga yajin aikin da suke yi, tare da yi wa masu tafiya a kafa kwace.

Jami’in hulda da jama’a na Rundunar  SP Abdullahi Haruna kiyawa ne ya bayyana hakan kamar yadda BBC Hausa ta rawaito a litinin din nan.

Tun dai da safiyar yau Litinin aka girke jami’an tsaro na ‘yan sanda da na rundunar tsaro ta civil Defense a wasu daga cikin manyan titunan Kano, don jiran ko ta kwana na yiwuwar samun rikici a lokacin da masu babur mai kafa uku a jihar kano suka fara yajin aiki.

A cewar SP Abdullahi Haruna Kiyawa, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Kano, mutanen da suka kama suna dauke da makamai inda suke tare hanya suna yi wa mutane kwace da tilasta wa masu kananan motoci daukar kaya sauke mutanen da suka dauko don rage musu hanya.

Kadaura24 ta rawaito dama al’ummar jihar kano sun yi hasashen samun irin wannan matsala ta kwacen waya ,wadda dama an dade ana kokawa da ita duk kuwa da kokarin da jami’an tsaro ke yi don magance matsalar.

1 COMMENT

  1. Allah sarki malam talaka ko yaushi Kai ne a wahala Dan sanda Dan karoto da sauran Jami,an tsaro babu Wanda ake takurawa Sai malam shehu

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...

An sake sauya lokacin jana’izzar Aminu Ɗantata – Gwamnatin Nigeria

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta ce Hukumomi a Kasar Saudiyyar...

Fadan daba: ku fito ku Kare Kan ku da iyayenku – Gwamnatin Kano ga matasa

Ku tashi ku Kare kanku da iyayen Gwamnatin jihar kano...