2023: Mai Nada Sarki  Zai Iya Zama Sarki – inji Tinubu

Date:

Daga Asiya Takalmawa
 Jagoran jam’iyyar APC na kasa, Bola Tinubu, ya yi watsi da kiraye-kirayen da ake yi a wasu bangarori na cewa ya kamata ya ci gaba da zama jagora a maimakon ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2023.
 Bola Tinubu ya bayyana hakan ne a lokacin da yake amsa tambayoyin manema labaran fadar shugaban kasa bayan wata ganawar sirri da suka yi da shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadar shugaban kasa ta Villa Abuja ranar Litinin din nan.
 A cewar jigon na jam’iyyar APC, shi dan Najeriya ne kuma yana da ‘yancin tsayawa takara da kansa, ba wai kawai ya tsaya matsayin jagora ba.
 “A ko’ina a duniya Ban taɓa ganin dokar da ta ce wai jagora ba zai tsaya takara ba sai dai ya tsaya a matsayin jagora, ba a haka don haka zan cigaba da neman Shugaban kasa kamar yadda na fadawa shugaba buhari ”. Inji Tinubu
 Jigon na jam’iyyar APC ya ce ya je fadar shugaban kasa ne domin sanar da shugaban kasa a hukumance bukatarsa ​​ta tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.
 Da aka tambaye shi ko shugaban kasar ya aminta da bukatar tasa,  Tinubu ya ce shugaban kasar bai  nemi ya ajiye bukatar tasa ba ta tsayawa takara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...