Bana Nadamar Goyon Bayan Ganduje da nayi har ya Zama Gwamna – Kwankwaso

Date:

Daga Zainab Muhd Darmanawa
 Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabi’u Kwankwaso, ya ce ba ya nadamar goyon bayan Gwamna Abdullahi Ganduje har ya zama Gwamnan jihar kano.
 A lokacin da Sanata Kwankwaso yake tattaunawa da gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi, ya yi jawabi game da dangantakarsa da Gwamna Ganduje a baya, da kuma yadda suka yi aiki tare har zuwa 2015.
 “Ba ni da wani nadama ko kadan saboda har yanzu muna da karfi, mun fi 2015 karfi. Ba wai a Kano kadai ba har ma a fadin kasar nan da ma wajen,” in ji shi.
 An fara zaben Kwankwaso a matsayin gwamnan jihar kano a shekarar 1999 kuma an sake zabersu a shekarar 2011, inda ya cika shekaru takwas da yana mulkin jihar kamar yadda kundin tsarin mulki ya ba shi dama.
 Lokacin da Ganduje ya zama gwamna, Kwankwaso a lokacin Sanata ne mai wakiltar Kano ta tsakiya a shekarar 2015.
 Duk da cewa an zabe shi a jam’iyyar PDP, mataimakinsa na lokacin, Abdullahi Ganduje, ya gaje shi a 2015 a matsayin dan takarar jam’iyyar APC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers Ta Mayar Da Martani Kan Sauke Alhaji Usman Daga Mukamin Wazirin Gaya

Daga Isa Ahmad Getso ‎ ‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers ta bayyana...

Rahoto: An kwantar da Buhari a ICU a Landan

  Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin...

Kacibus: A karon farko an hadu tsakanin Gwamnan Abba da Sarki Aminu Ado a Madina

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   A karon farko an hadu tsakanin...

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...