Gwamnatin Taliban Za ta Fara Zane Waɗanda Su Ka Je Masallacin Juma’a a Makare a Kasar Afghanistan

Date:

 

Gwamnatin Taliban, a ƙasar Afghanistan ta sanar da wata sabuwar doka da ta shafi dukkan al’ummar kasar.

Dokar ta baiyana cewar, da ga yanzu duk wanda ya makara bai je masallacin Juma’a ba har a ka fara Huɗuba, to za a yi masa bulala 25.

Dokar ta ce hukuncin babu babba, babu yaro, in da gwamnatin ta ce “saboda haka hukumomin Gwamnatin Taliban su ke kira ga dukkan al’ummar ƙasar Afghanistan da su kiyaye wannan doka, wajen zuwa Masallacin Juma’a akan kari.”

Daily Nigerian ta rawaito Gwamnatin ta baiyana cewar dokar za ta fara ne daga gobe Juma’a, shi ya sa ma a ka shiga kasuwanni ana sanar da jama’a dokar a yau.

A gefe guda kuma, Gwamnatin ta samar da isassun bulalai ga dukkan jami’an tsaro da za su bi layi-layo don hukunta masu kunnen ƙashi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...