Daga Rabi’u Sani Hassan
Majalisar matasan Nigeria wato Youths Assembly of Nigeria reshen jihar Zamfara ta bukaci gwamnatin jihar da ta samar da muhimman tsare-tsare don inganta rayuwar matasan jihar domin samun makoma mai kyau ga matasan.
Kadaura24 ta rawaito Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka raba manema labarai mai dauke da sa hannun shugaban Kungiyar Mahmud A. Lawal, a cikin sanarwar Majalisar ta zargi gwamnatin jihar da taka muhimmiyar rawa wajen koma bayan da matasan jihar ke samu, sakamakon shakulatin bangaro da tayi da fannonin ci gaban su a 2021 data gabata.
Lawal yace a wannan shekarar ma hakan ka iya faruwa kuma zai zarce abun da ya faru a shekarar data gabata, duba da rashin wani muhimmin tanadi da gwamnatin ta yiwa matasan a cikin kunshin kasafin kudin shekarar 2022.
Ya kara da cewa ya kamata gwamnatin jihar ta dauki kwararan matakai wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ýan kasa tare da samar da kyakkyawar makoma ga dubban daruruwan matasan jihar don gujewa gagarumar matsalar da ka iya tasowa nan ga a tsakanin matasan jihar.
Sanarwa tace kawo yanzu matasa da dama na fuskantar matsaloli da kalubale ta fuskoki da dama musamman yadda ýan bindiga suka addabi alúmmar jihar abinda yayin sandiyyar gurgunta harkokin tattalin arziki da tabarbarewar yanayi harkokin noma da Kasuwanci a Jihar.
Daga bisani shugaban matasan yace matsalar da harkar noma ta samu a jihar ya taka rawa sosai wajen rage yawan matasan dake iya samun damar shiga makarantun gaba da sakandire a jihar.
I pay a visit each day a few web pages and sites to read
posts, except this blog provides feature based articles.