Gidauniyar tallafawa marayu ta tukuntawa ta rabawa marayu 50 kayan karatu da uniform

Date:

Daga Umar Mai Hula

Anyi Kira ga Al ummar musulmi dasu Mai da hankali wajen tallafawa marayu musamman a wannan hali da ake ciki.

 

Wannan Kiran yafito ne daga bakin Malam Muhammad yunusa Limamin unguwar tukuntawa a lokacin daya ke jawabi a wajen raba kayan karatu ga Marayu Guda 50 Waɗanda Gidauniyar tallafawa marayu ta Tukuntawa ta Gudanar.

Muna tallafawa Mata da Marayu ne don inganta Rayuwar su – Baba Yawale

Malam Muhammad yace akwai lada Mai tarin yawa da Allah yayi tanadi ga Waɗanda suke tallafawa marayu, Inda tallafawa marayu na Kara imani da Kuma Kara kusanci ga Allah.

 

Anasa jawabin shugaban kungiyar Yakubu Abubakar yace abin da yasa suka raba kayan karatun shi ne sabo da mahinman cin da karatu yake dashi a halin yanzu.

 

Yace Babu abun da zaka baiwa Mutum ka taimake shi3a Wannan Lokaci kamar karatu, yace shi yasa Muka Raba musu Waɗannan Kayan don su ji dadin yin karatunsu ba tare da Wani tarnaki ba.

Malam Yakubu yace da Gidauniyar su day dade da yin nisa wajen tallafawa marayu,Kuma ya Sha alwashin zasu cigaba da yin duk mai yiwuwa wajen tallafawa marayun don inganta Rayuwar su.

Suma marayun da suka rabauta da kayan karatun sunyiwa kungiyar fatan Al kairi da kuma Samun nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...