Malamin Jami’ar MAAUN Ya Bukaci Masu Bincike Su Samar Da Bincike Mai Inganci Don Haɓɓaka Ilimin Duniya

Date:

Daga Ali kakaki

Wani Malami a Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijer (MAAUN), Farfesa Ahmad Maigari Ibrahim, ya shawarci masu bincike da su gabatar da ayyuka masu inganci a cikin mujallu wanda zasu yi tasiri don haɓaka ilimin duniya.

KADAURA24 ta rawaito Farfesa Maigari Ibrahim ya ba da wannan shawarar ne a wani muhimmin jawabi da ya gabatar a wajen taron kasa da kasa na farko kan hanyoyin ladabtarwa, wanda ya gudana a Kano .

Taken taron shi ne: “Ci gaban Ilimi a matsayin magani da barazanar rashin tsaro tare da mai da hankali kan ‘yan gudun hijirar (IDPs): Hanyar ladabtarwa mai yawa.”

Ya ce shawarar ta zama wajibi domin bunkasa ilimin duniya don karfafa ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin duniya baki daya.

Babban mai gabatar da kasida a wajen taron, Dakta Habib Awais Abubakar ya gabatar da takarda mai taken: “Ƙasashen Duniya, Adabi da Ingantacciyar hanyar Koyarwar Jami’a a Ƙarni na 21” wadda aka rubuta tare da Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, wanda ya kafa kuma shugaban rukunin jami’o’in MAAUN.

A yayin taron, masu bincike na duniya sun gabatar da takardun bincike masu inganci guda 36 a yayin da sama da mahalarta 70 suka halarci taron.

Shi ma a na sa jawabin, Farfesa Muhammad Rayyan Garba ya taya mahalarta taron murna tare da jaddada muhimmancin taron ga malaman jami’o’in kasar nan.

Babban mai masaukin baki a taron, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, wanda shi ne kuma wanda ya kafa kuma shugaban Jami’ar MAAUN kuma shugaban kungiyar jami’o’in masu zaman kansu na Afrika wanda ya halarci taron ta hanyar Intanet daga kasar Faransa, ya taya mahalarta taron murna tare da jaddada aniyarsa wajen inganta ingantaccen ilimi a Afirka da sauran kasashen waje.

A jawabin rufe taron, Magatakardar MAAUN, Shu’aibu Usman Tanko ya yabawa shugaban Jami’ar kuma wanda ya kafa jami’ar, Farfesa Adamu Abukakar Gwarzo, da kwamitin shirya taron, baki da masu gabatar da jawabai, masu lura da taro da sauran mahalarta taron bisa gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar gudanar da taron.

Taron wanda ya gudana a ranekun 16 da 17 ga watan Disambar 2021 ta hanyar Intanet, duk da haka kwamitin shirya taron da wasu daga cikin masu gudanar da taron sun hadu a zahiri a babbar cibiyar taro ta Amani Event Centre da ke Kano domin gudanar da taron ta Intanet.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...