Yan Sanda a Katsina sun ce sun kama Mutum daya Cikin Waɗanda ake zargi da kisan Kwamishina a Jihar

Date:

Rundunar Yan Sanda a Jihar Katsina ta tabbatar da kisan gillar da aka yiwa kwamishinan kimiya da fasaha na Jihar Dr Rabe Nasir a gidan sa dake rukunin gidajen Fatima Shema a birnin Katsina, yayin da suka ce an kama mutum guda da ake zargi da aikata kisan.

Wannan ya biyo bayan ziyarar gidan sa da kwamishinan ‘Yan Sanda Sanusi Buba da Daraktan DSS suka yi, sakamakon samun labarin.

Rahotanni sun ce an dabawa kwamishinan wuka ne a ciki a cikin gidan sa, yayin da aka janye gawar sa zuwa ban daki inda aka kulle ta.
Kwamishinan ‘Yan Sanda Buba yace a daren jiya laraba aka kashe kwamishinan amma kuma sai yau alhamis aka samu gawar, yayin da yace an kama mutum guda da ake zargin yana da hannu wajen kisan.
Buba yace an dauki gawar kwamishinan zuwa Cibiyar kula da lafiya dake Katsina.
Bayanai sun ce jami’an tsaro sun samu wayar kwamishinan tare da wata da ake kyautata zaton na wanda ya hallaka shi ne.
Gwamnan Jihar Aminu Bello Masari na daga cikin wadanda suka ziyarci gidan kwamishinan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...