Ba Ranar da ba a Kashe Mutum a Arewacin Nigeria – Sarkin Musulmi

Date:

Sarkin Musulmin Najeriya Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar na ukku ya shawarci ‘yan Najeriya da su hada kansu don kawo karshen ta’addanci a kasar.

A lokacin da yake tsokaci kan matsalar tsaro a Najeriya a taron majalisar hadin kan addinai ta NIREC, Sultan Sa’ad Abubakar ya ce ba lokaci ba ne da mabiya addinai musamman Musulmi da Kirista za su rika zargin juna da yi wa juna barazana ba.

Sarkin Musulmin ya nuna damuwa kan yadda kashe-kashe da sace-sacen jam’a ke ci gaba da afkuwa, amma kuma Musulmi da Kirista sun bige da nuna wa juna yatsa da yi wa juna barazana.

” Dole ne mu daina zargin juna kuma mu hada kai matsawar muna son mu yaki makiyanmu. Idan na ce zan yi magana kan rashin tsaro a arewa babu lokacin da za mu bar dakin taron nan. In ji Sultan.

Yakara da cewa , “yan kwanakin da suka wuce mun karanta a jaridu yadda aka kona matafiya a bas a Sokoto. Babu ranar da za ta zo ta wuce ba a kashe mutane a Arewa ba, musamman Arewa maso Yamma.”

Bugu da kari Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar ya bukaci shugabanni da sauran hukumomin tsaro su hada kai su kuma fahimci girman matsalar tare da magance ta.

“Kar mu yaudari kanmu, abubuwa ba sa tafiya yadda yakamata a Najeriya. Na sha fada a lokuta da dama cewa abubuwa ba sa tafiya yadda ya kamata. Kuma idan dai kasan matsalarka, magance ta ba zai yi maka wahala ba. Saboda haka ya kamata mu san na yi kafin lokaci ya kure mana

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...