Amfani da karfin Soji ba Zai Kawo Zaman lafiya a Africa ba – Abdulsalam Abubakar

Date:

Tsohon shugaban Najeriya, Janar Abdulsalami Abubakar (rtd), ya ce dole ne kasashen Afirka su sauya salon da suke amfani da shi wajen wanzar da zaman lafiya yana mai cewa amfani da karfin soji ba zai kawo lumana ba.

Ya bayyana haka ne a Abuja ranar Asabar a wani taro da aka gudanar domin karrama shi.

Abubakar ya ce har yanzu nahiyar Afirka na fama da rikice-rikice “iri daban-daban,” wadanda ya ce suna ciki manyan kalubalen da ke addabar nahiyar.

BBC Hausa ta rawaito Jaridar ThisDay, wadda ta ambato shi yana wadannan kalamai ta ce tsohon shugaban kasar ya bukaci shugabannin Afirka su rungumi “sasantawa da yin sulhu” wajen magance rikici-rikice.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...