Gwamna Tambuwal yasa Hannu a Dokar Kare hakki Kananan Yara a Sokoto

Date:

Daga Junaidu Sani
  Gwamna Aminu Waziru Tambuwal na jihar Sokoto ya sanya hannu kan dokar kare hakkin yara da nufin inganta rayuwar yara a jihar.
  Da yake jawabi bayan zartar da dokar, Gwamnan ya bayyana dokar a matsayin daya daga cikin manyan nasarorin da gwamnatin sa ta samu.
 Kadaura24 ta rawaito cewa Gwamnan ya kuma sanya hannu kan dokar hana cin zarafin Bil Adama wadda ta tanadi kawo karshen duk wani nau’i na cin zarafin mata a jihar.
 An rattaba hannu kan dokar ne a wani gagarumin biki da ya samu halartar jami’in kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya, Edward Kallon, da babban jami’in UNICEF a Sokoto, Mista Maulid Warfar, wakilin Plan International da dai sauransu.
 Da yake jawabi, Mista Edward Kallon ya yaba da jajircewar Gwamna Tambuwal da sauran hukumomi da dai-daikun Mutane wajen tabbatar da kafa dokar tare da yin kira ga sauran Jihohin kasar nan da su yi koyi ga Gwamnatin Jihar Sakkwato wajen zartar da dokokin da suka tabbatar da ‘yancin mata da yara.
 Kallon ya ka da cewa EU-UN Spotlight Initiative Project an tsara shi ne don haɓaka haƙƙin daidaikun mutane da tabbatar da yanayin ingantacciyar rayuwar mutane daga kowane nau’i na cin zarafi da ƙarfafa gwaiwar mata da ‘ya’ya mata da ƙwarewar rayuwa a cikin al’umma.
  Gwamnan ya yabawa majalisar dokokin jihar da kwamishinan shari’a Suleiman Usman SAN da kwamishiniyar harkokin mata da yara Hajiya Kulu Sifawa bisa kokarinsu na ganin kudurin ya yi daidai da jahohi ya tanadi ka’idoji da dabi’u na al’adu da addini.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...