Bayan Kama Wasu Matasa Suna Karta, Hukumar Hisbah a Kano ta raba musu ƙur’ani su karanta

Date:

 

Dakarun Hisba sun kama wasu matasa yayin da su ke tsaka da wasan katin ‘Whot’

A wata taƙaitacciyar sanarwa da ta wallafa a sahfinta na facebook, rundunar ta ce jami’an ta na Ƙaramar Hukumar Warawa ne su ka kama matasan su na cikin yin wasan katin ‘Whot’ ɗin.

Daily Nigeria ta rawaito Sanarwar ta ce rundunar, a ƙarƙashin jagorancin Babban Kwamanda, Dakta Muhammad Haroon Ibn Sina, ta kama matasan ne sakamakon su na ɓata lokacinsu, maimakon su yi wani abu mai amfani.

Sanarwar ta ƙara da cewa bayan dakarun sun kama matasan, sai su ka rarraba musu wani sashe na ƙur’ani mai tsarki domin su yi taƙara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...

An sake sauya lokacin jana’izzar Aminu Ɗantata – Gwamnatin Nigeria

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta ce Hukumomi a Kasar Saudiyyar...

Fadan daba: ku fito ku Kare Kan ku da iyayenku – Gwamnatin Kano ga matasa

Ku tashi ku Kare kanku da iyayen Gwamnatin jihar kano...