Nasiba Rabi’u Yusuf
Shugaban karamar Hukumar Kumbotso Hon Hassan Garban kauye farawa ya Aike da sakon Ta’aziyya ga Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da masarautar Kano karaye da Kuma Al’ummar Jihar Kano Bisa Rasuwar Sarkin Tsaftar Kano Alhaji Jafaru Ahmed Sani Gwarzo.
Shugaban karamar Hukumar ta Kumbotso yace Za’a Dade ana tunawa da irin gudunmawar da Marigayin ya bayar wajen cigaban jihar Kano, musamman ta fuskar Kiwon lafiya. Da yake Mika sakon Ta’aziyya Alhaji Hassan farawa yai fatan Allah Swt ya jikansa yakai Rahama kabarinsa.
“innalillahi wa innalillahir Raji’un, Babu Shakka munyi Babban Rashi da fatan Allah Swt ya jikansa ya Kuma Baiwa Iyalai, yan Uwa da Al’ummar jihar kano Hakurin jure Rashi” a cewar Garban kauye.
Farawa ya Aike da sakon Ta’aziyya ne kai tsaye daga kasar Saudia Amadadin Al’ummar karamar Hukumar Kumbotso, Cikin wata sanarwa da Mai Taimakamasa kan harkokin yada labarai Shazali farawa ya sanyawa Hannu.
Kafin Rasuwarsa dai Gwarzo, ya kasance Babban mataimaki na musamman ga Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje Kan Tsaftar .