Tsaftar Muhalli: Kano zata dade Bata Manta da Sarkin Tsaftar Kano ba – Garban Kauye

Date:

Nasiba Rabi’u Yusuf
Shugaban karamar Hukumar Kumbotso Hon Hassan Garban kauye farawa ya Aike da sakon Ta’aziyya ga Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da  masarautar Kano karaye da Kuma Al’ummar Jihar Kano Bisa Rasuwar Sarkin Tsaftar Kano Alhaji Jafaru Ahmed Sani Gwarzo.
Shugaban karamar Hukumar ta Kumbotso yace Za’a Dade ana tunawa da irin gudunmawar da Marigayin ya bayar wajen cigaban jihar Kano,  musamman ta fuskar Kiwon lafiya. Da yake Mika sakon Ta’aziyya Alhaji Hassan farawa yai fatan  Allah Swt ya jikansa yakai Rahama kabarinsa.
“innalillahi wa innalillahir Raji’un, Babu Shakka munyi Babban Rashi da fatan Allah Swt ya jikansa ya Kuma Baiwa Iyalai, yan Uwa da Al’ummar jihar kano Hakurin jure Rashi” a cewar Garban kauye.
Farawa ya Aike da sakon Ta’aziyya ne kai tsaye daga kasar Saudia Amadadin Al’ummar karamar Hukumar Kumbotso, Cikin wata sanarwa da Mai Taimakamasa kan harkokin yada labarai Shazali farawa ya sanyawa Hannu.
Kafin Rasuwarsa dai Gwarzo, ya kasance Babban mataimaki na musamman ga Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje Kan Tsaftar .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...