Buhari ya Amince a baiwa Kowacce Jiha tallafin Naira Biliyan 18

Date:

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya amince da bai wa jihohin ƙasar 36 tallafin naira biliyan 656.112.

Bayanan tallafin sun fito ne yayin taron Majalisar Tattalin Arziki ta Ƙasa wanda Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo ya jagoranta ranar Alhamis.

Wata sanarwa daga ofishin Mista Osinbajo ta ce kowace jiha za ta samu naira biliyan 18.225, wanda za ta biya cikin shekara 30 kan kuɗin ruwa kashi 9 cikin 100.

A cewar fadar shugaban ƙasa, an ɗauki matakin ne saboda a tallafa wa jihohi cimma muradansu na harkokin kuɗi musamman kasafin kuɗaɗensu na shekara.

Za a raba kuɗin ne a mataki shida cikin wata shida kuma ta hannun Babban Bankin Najeriya (CBN) za a rarraba wa jihohin.

Tun a watan Yuli ne Ministar Kuɗi Zainab Ahmad ta faɗa wa majalisar cewa za a fara zarar kuɗi daga asusun jihohin domin fara biyan bashin tallafin farko da aka ba su, amma sai jihohin suka nuna turjiya tare da neman wani agajin, abin da ya sa aka ɓullo da agajin kasafin kuɗin kenan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...