An sace tsohon Shugaban tashoshin Jiragen Ruwa a Kano

Date:

Rahotanni a jihar Kano na cewa ‘yan bindiga sun sace wani tsohon Janar-Manaja na hukumar kula da tashoshin jiragen ruwa, NPA.

Bayanai sun nuna cewa an sace Bashir M Abdullahi daga gonarsa da ke kauyen Sitti na karamar hukumar Sumaila ranar Laraba da almuru.

BBC Hausa ta rawaito rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ba ta da labarin sace mutumin kawo yanzu.

Amma bayanai sun nuna cewa ‘yan bindigar sun rika fakon mutumin ne har suka kai ga sace shi.

Hakan na faruwa ne a yayin da rahotanni suke cewa wasu ‘yan bindigar da suka tsere daga jihohin Katsina da Zamfara da kuma Sokoto – wadanda suke fama da matsalolin tsaro – sun fara samun mafaka a wasu yankuna na jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...