Da dumi-dumi: Zamu karbi korafin zaben APC da akai a Sani Abacha ne Kawai – APC ta kasa

Date:

Daga Sani M Sadeeq

Kwamitin karbar korafe-korafen zaben Shugabannin APC na jihohin da Uwar jam’iyyar APC ta Kasa ta  aiko nan Jihar Kano ya Fara Zama a Ranar asabar din nan domin karbar korafe-korafen ‘ya’yan jam’iyyar Dangane da zaben.

Kadaura24 ta rawaito Shugaban Kwamitin Dr Tony Macfoy yace Kwamitin Zai karbi korafin Waɗanda suka shiga zaben da aka gudanar a filin Wasa Sani Abacha ne Kawai Saboda shi uwar jam’iyyar ta Sani.
Yace Kwamitin Zai kawashe kimanin kwanaki uku yana Zama domin karbar korafe-korafen ,Wanda Zai Fara daga yau asabar zuwa Ranar litinin Mai zuwa, Inda yace zasu Rika Zama ne daga karfe goma na safe zuwa karfe hudu na Yamma.
Dr Tony yace su basu San da Wani zabe da akai a Wani waje ba a Kano bayan wanda aka gudanar a filin Wasa na Sani Abacha Saboda shi Jami’an uwar jam’iyyar APC ta Kasa Suka halarta har Suka saka da Rahoton su.
” Uwar jam’iyyar APC tasan da Wani zabe da akai Bayan wancan da kwanitoci biyu zata turo ,Amma Yanzu mu kadai aka turo Kano.
Kwamitin Mai Mutane 5 dai yana Zama ne a sakatariyar jam’iyyar APC ta Jihar Kano dake Kan titin Maidugu a birnin Kano.
Idan ba’a mantaba a ranar Asabar din data gabata ne aka gudanar da zabuka biyu na Shugabanin jam’iyyar APC a Kano Wanda ya Samar da Abdullahi Abbas da Alhaji Ahmadu Haruna zago a Matsayin Shugabanin bangarorin jam’iyyar biyu a kano

3 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...