Bani da zabin da ya wuce tallafawa al’ummar da suka zabeni – Kabiru Dan-Hassan

Date:

Daga Sufyan Dantala Jobawa
Dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kura, madobi da Garun mallam, Kabiru Idris Dan-Hassan ya bukaci shugabanni da ma gwamnatoci da su samar da tsarin tallafawa al’umma a wannan lokaci da aka shiga matsin rayuwa da tsadar kayayyaki.
Dan majalisar ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ke mika na’urorin rarraba hasken wutar -lantarki wato(Transformers) da kuma na’urorin samar da hasken wutar lantarki masu aiki da hasken rana ga al’ummomin da ya ke wakilta.
Yace la’akari da yanayin da ake ciki ya zamarwa Shugabani dole su Shigo Cikin al’ummar su domin tallafa musu su fita daga Cikin mawuyacin halin da ake ciki.
Kabiru Idris Dan-Hassan wanda Bello Datti Kura, ya wakilce ya bukaci mawadata da su rinka tallafawa masu karamin karfi a tsakanin al’umma domin rage musu radadin talauci da ake fama dashi.
Daga bisani Dan Majalisar ya kuma ba da tabbacin tallafawa bangaren lafiya da sauran fannonin cigaban rayuwar al’umma, inda ya ce yana baiwa aiyukan raya kasa fifiko da nufin cigaban mutanen da ya ke wakilta.
Shi ko a nasa bangaren, shugaban karamar hukumar Garun mallam Mudansur Aliyu Dakasoye wanda ya yi jawabi a madadin sauran takwarorinsa sun bada tabbacin wayar da kan al’umma domin kulawa da kayayyakin da aka samar musu don inganta rayuwar su.
Daga cikin wuraren da suka amfana sun hadar da kofar yamma a garin Kura da Garin Yanaba dake karamar hukumar Garun mallam, sai kuma cikin garin madobi a karamar hukumar madobi.

1 COMMENT

  1. Agaskiya hakane afada achika Sai Dan kunya transformer tazo yanaba Dan àllah katai maka a janyo way zuwa tsaure nagode daga surajo tsaure

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...