Na Warke sosai, yanzu Babu abun da yake damu na-Bola Tinubu

Date:

Jagoran jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, Asiwaju Bola Tinubu, ya dawo ƙasar nan bayan ya shafe wata kusan huɗu a birnin Landan sakamakon jinya.

Cikin wata sanarwa daga ofishin yaɗa labaransa a ranar Juma’a, Tinubu ya ce ya warke sarai tare da musanta “jitar-jitar da ake yaɗawa” kan rashin lafiyar tasa.

Ta ƙara da cewa an yi masa tiyata ne a gwiwarsa ta dama da kuma ba shi kulawar bayan tiyata.

“Mai girma Asiwaju Bola Tinubu ya sauka ne ranar Juma’a 8 ga watan Oktoba da yamma daga Landan,” a cewar sanarwar.

“Saɓanin abin da ake yaɗawa, ba a yi masa wata tiyata ba saɓanin wannan sannan kuma babu shirin yi masa wata nan gaba. Ya warke a kan lokaci kuma ba tare da wata matsala ba.”

Cikin sanarwar, Tinubu ya gode wa Shugaba Muhammadu Buhari “saboda ziyartarsa da ya yi a Landan” da gwamnoni da ‘yan majalisar yankin Arewa da ‘yan majalisar Jihar Legas.

An sha alaƙanta Bola Tinubu da neman takarar shugaban ƙasa a Najeriya, sai dai har yanzu dattijon mai shekara 69 kuma tsohon gwamnan Legas bai bayyana sha’awarsa ba ƙarara.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tsofaffin Kansiloli Sun Yi Saukar Alƙur’ani da Addu’a na Musamman ga Gwamna Abba

  Ƙungiyar tsofaffin kansiloli na jihar Kano ta gudanar da...

Hisbah ta kama mutane 25 bisa zargin shirya auren jinsi a Kano

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama akalla mutane...

Yadda ƴansanda suka kama wasu da suke zargin ƴanbindiga ne a Kano

Rundunar yansanda ta Kasa reshen jihar Kano ta ce...

Rikici a Bebeji: Jigon Kwankwasiyya na zargin an shirya cire sunayen tsoffin kansiloli domin yin kashe-muraba

Wani jigo a tafiyar Kwankwasiyya a karamar hukumar Bebeji...