Kwamishinan Yan Sanda a Kano ya yaba da Gudummawar yan Kanywood a bangaren tsaro

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman

Rundunar Yan Sanda ta Kasa reshen jihar Kano tasha alwashin cigaba da bada Gudunmawar ta ga Masana’atar Shirya fina-finan Hausa ta Kannywood Saboda da irin Gudunmawar da suke bayarwa wajen inganta harkokin Tsaro a jihar Kano.

Kwamishinan Yan Sanda reshen jihar Kano CP Sama’ila Shu’aibu Dikko ne ya bayyana hakan Yayin daya karbi bakuncin Kungiyar Matan Kanywood da Kuma tawagar mashiryin rishirin fin din A Duniya Taijjani Asase Kamar yadda Jami’in hulda da Jama’a na Rundunar DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya Sanar Cikin Wata sanarwa da ya fitar.

Kwamishinan yace Yan wasan Hausan Suna bada tasu Gudunmawar wajen inganta tsaro ta Hanyar wayar da Kan al’umma da Kuma ilimantar da su Dangane da harkokin tsaro.

“Sha’anin tsaro Abu ne Daya Shafi kowa don haka muke Bukatar ku cigaba da bada kyakykyawar Gudunmawar da kuke bayarwa don inganta tsaro, Ina baku tabbacin Rundunar mu zata cigaba da Mara Muku baya a aiyukan da kuke na fadakar da al’umma.”Inji CP Sama’ila Dikko

Da yake nasa Jawabin Shugaban Kamfanin dake Shirya fun din a Duniya Taijjani Asase yace sun je ofishin Kwamishinan domin bashi tabbacin zasu cigaba da bada Gudunmawa a fina-finan su wajen nuna darajar Yan Sanda.

Ya ce zasu cigaba da nuna kyakykyawan halayen Yan Sanda da Kuma nuna Hanyoyin da za’a Magance Matsalar tsaro a unguwanni da Sauran garuru.

Tijjaniya Asase yace zasu gyara duk kura-kuran da suke yi a fina-finansu a sha’anin da ya Shafi tsaro da aiyukan Yan Sanda.

17 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba gaskiya a bayanin wasu Manoman Kano da suka ce Muna karbar kudi a wajensu – Civil defense

Rundunar tsaro ta Civil defense ta Kasa reshen jihar...

Korar ma’aikata a Kano: Bashir Gentile ya yiwa Faizu Alfindiki martani mai zafi

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Masanin kimiyar siyasa kuma mai sharhi...

Sakataren kungiyar NRO Abdulkadir Gude ya rasu

Allah ya yi wa dattijo, kuma Sakataren kungiyar Northern...

Gwamnatin da ta ke korar Ma’aikata ba ta Cancanci Wa’adi na biyu ba – Faizu Alfindiki

Daga  Maryam Muhammad Ibrahim   Abin takaici ne ganin yadda gwamnatin...