Da dumi-dumi : Ganduje ya Sanar da Sunan Sabon Sarkin Gaya

Date:

Daga Usman Hamza

Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya Amince da nadin Alhaji Aliyu Ibrahim Gaya a Matsayin Sabon Sarkin Masarautar Gaya, bayan rasuwar Mai Martaba Sarkin Alhaji Ibrahim Abdulkadir.

Sakataren Gwamnatin jihar Kano Alhaji Usman Alhaji ne ya bayar da Sanarwar a madadin gwamnatin jihar Kano.

Kadaura24 ta rawaito cewa gabanin bayar da Sanarwar Sabon Sarkin, sai da Masu zabar Sarki a Masarautar Gaya suka gudanar da aikinsu na zabar Sarki kafin daga bisani gwamnan Kano ya Amince da Sabon Sarkin na Gaya.

Gwamna Ganduje ya zabi Alhaji Aliyu Wanda da shine ciroman Gaya Kuma babban da ga Marigayi Sarkin Gaya Alhaji Ibrahim Abdulkadir na cikin Mutane uku da Masu zabar Sarki a Masarautar suka gabatar Masa a Matsayin Waɗanda suka zaba

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito Marigayi Mai Martaba Sarkin Gaya Alhaji Ibrahim Abdulkadir ya Rasu a Ranar Larabar nan data gabata.

39 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...