Gwamnatin Kano ta sauyawa makarantar mata ta Mai Kwatashi matsugunni

Date:

Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano ta ɗauke Karantar Sakandare ta Mata ta Mai Kwatashi daga titin France Road, Sabongari zuwa unguwar Kaura Goje a karamar hukumar Nassarawa.

Freedom Radio ta rawaito cewa Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ne ya bada umarnin sakewa makarantar matsuguni biyo bayan koken ƴan unguwar Kaura Goje da kewayenta akan zargin yadda ake wa ɗaliban makarantar kwace da sauran su.

Tuni dai kungiyar cigaban unguwannin Kaura Goje, Gwagwarwa, Gawuna, Riga, da Gamar Fulani ta mika sakon godiya ga Gwamna Yusuf bisa cika alƙawarin sauyawa makarantar.

Mazauna unguwannin sun nuna farin ciki yadda aka kai makarantar kusa da su, musamman ma ganin cewa ta mata ce, inda su ka nuna cewa hakan zai kara habaka ilimin mata a yankin nasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...