Na yi Matukar Kaduwa da Rasuwar Sarkin Gaya – Sanata Kabiru Gaya

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam

Sanatan Kano ta kudu Sanata Kabiru Ibrahim Gaya ya bayyana matukar kaduwarsa da rasuwar Mai Martaba Sarkin Gaya Alhaji Ibrahim Abdulkadir a Ranar Larabar nan.

Sanata Kabiru Gaya ya bayyana hakan ne Cikin Wani sakon ta’aziyya da ya Sanyawa Hannu Kuma ya aikowa Kadaura24.

Sanata Gaya yace Rashin Sarkin Babban rashi ne ba ga al’ummar Masarautar Gaya kadai ba ,har da jihar Kano da Nigeria baki Daya.

” Mai Martaba ya taimaki al’umma sosai tun da kuruciyarsa Lokacin yana Abuja ya samarwa Mutane aiyukan yi Kuma har ya zama Sarki Bai daina ba. Kuma da ya Zama Sarki Mai cikakken iko yayi iya Bakin kokarin wajen Samar da Zaman lafiya bunkasa Ilimi lafiya da dai Sauransu.” Inji Sanata Kabiru Gaya

” Alhaji Ibrahim Abdulkadir mutumin kirkine Wanda ya sadaukar da Rayuwarsa wajen hidimtawa al’ummar sa da Kawo Cigaba yankinmu Kuma ya taima sosai wajen inganta Rayuwar Al’ummarsa”. Inji Sanata Gaya

Sanata Gaya ya Mika Sakon ta’aziyyar ga Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da Sarakunan jihar Kano da al’ummar Masarautar Gaya da na Kano Baki daya

Yayi addu’ar Allah ya gafartawa Mai Martaba Sarkin yasa Yana aljanna ya Kuma kyautata makwancinsa .

18 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...