Na yi Matukar Kaduwa da Rasuwar Sarkin Gaya – Sanata Kabiru Gaya

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam

Sanatan Kano ta kudu Sanata Kabiru Ibrahim Gaya ya bayyana matukar kaduwarsa da rasuwar Mai Martaba Sarkin Gaya Alhaji Ibrahim Abdulkadir a Ranar Larabar nan.

Sanata Kabiru Gaya ya bayyana hakan ne Cikin Wani sakon ta’aziyya da ya Sanyawa Hannu Kuma ya aikowa Kadaura24.

Sanata Gaya yace Rashin Sarkin Babban rashi ne ba ga al’ummar Masarautar Gaya kadai ba ,har da jihar Kano da Nigeria baki Daya.

” Mai Martaba ya taimaki al’umma sosai tun da kuruciyarsa Lokacin yana Abuja ya samarwa Mutane aiyukan yi Kuma har ya zama Sarki Bai daina ba. Kuma da ya Zama Sarki Mai cikakken iko yayi iya Bakin kokarin wajen Samar da Zaman lafiya bunkasa Ilimi lafiya da dai Sauransu.” Inji Sanata Kabiru Gaya

” Alhaji Ibrahim Abdulkadir mutumin kirkine Wanda ya sadaukar da Rayuwarsa wajen hidimtawa al’ummar sa da Kawo Cigaba yankinmu Kuma ya taima sosai wajen inganta Rayuwar Al’ummarsa”. Inji Sanata Gaya

Sanata Gaya ya Mika Sakon ta’aziyyar ga Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da Sarakunan jihar Kano da al’ummar Masarautar Gaya da na Kano Baki daya

Yayi addu’ar Allah ya gafartawa Mai Martaba Sarkin yasa Yana aljanna ya Kuma kyautata makwancinsa .

18 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...