Mun haramta nunawa ko sayar fim din da ake Garkuwa da Mutane a Cikin sa – Afakallah

Date:

Daga Aisha Muhd adam

Hukumar Tace Finafinai ta jihar Kano, ta haramta nunawa ko sayar da fina -finan da ke nuna garkuwa da mutane, shan muggan kwayoyi da kwacen wayoyi a Cikin su a jihar Kano.

Sakataren zartarwa na hukumar, Ismaila Naaba Afakallah, ya bayyana cewa haramcin ya zama tilas, saboda abubuwan da ake magana yanzu sun zama sanannu a tsakanin Jama’a Kuma suna taimakawa Bata gari.

“Daga yanzu, ba za mu amince da fina -finan da ke nuna garkuwa da mutane ba, shan muggan kwayoyi da wayoyin GSM wanda yanzu ya yi wa al’ummar jihar Kano illa”.

Afakallah ya bayyana cewa an dauki matakin ne don takaita barazanar da kuma rage yiwuwar matasa su yi amfani da Hanyoyin wajen shiga aiyukan da basu dace ba.

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...

Kananan Hukumomin Tarauni Rogo da Doguwa sun zamo koma baya wajen yin rijistar Masu zabe a Kano

Rahotanni sun nuna cewa ya zuwa yanzu kananan hukumomin...