Mun haramta nunawa ko sayar fim din da ake Garkuwa da Mutane a Cikin sa – Afakallah

Date:

Daga Aisha Muhd adam

Hukumar Tace Finafinai ta jihar Kano, ta haramta nunawa ko sayar da fina -finan da ke nuna garkuwa da mutane, shan muggan kwayoyi da kwacen wayoyi a Cikin su a jihar Kano.

Sakataren zartarwa na hukumar, Ismaila Naaba Afakallah, ya bayyana cewa haramcin ya zama tilas, saboda abubuwan da ake magana yanzu sun zama sanannu a tsakanin Jama’a Kuma suna taimakawa Bata gari.

“Daga yanzu, ba za mu amince da fina -finan da ke nuna garkuwa da mutane ba, shan muggan kwayoyi da wayoyin GSM wanda yanzu ya yi wa al’ummar jihar Kano illa”.

Afakallah ya bayyana cewa an dauki matakin ne don takaita barazanar da kuma rage yiwuwar matasa su yi amfani da Hanyoyin wajen shiga aiyukan da basu dace ba.

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...