Yanzu-Yanzu :Ganduje ya Rushe Hukumar Remasab

Date:

Daga Sani Magaji Garko

Gwamnatin jihar Kano ta rushe hukumar kwashe shara da tsaftar Muhalli ta jihar Kano wato REMASAB.

Kwamishinan muhalli Dakta Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan yayin zantawarsa da ‘yan jaridu.

Ya ce gwamnatin Kano ta rushe hukumar, sai dai babu wani ma’aikaci ɗaya da zai rasa aikin sa, domin kuwa an yi tsarin rarraba ma’aikatan hukumar zuwa wasu hukumomin, su kuwa ma’aikatan wucin gadi an mikawa wani kamfanin Wanda suka sanya Hannu kan yarjejeniya da shi.

Ya ce, tuni gwamnati ta dauki matakin sauya salon sarrafa shara ta hanyar hadin guiwa da wani kamfani mai zaman kan sa da zai rika sarrafa shara, don ta zamo takin zamani da iskar gas da kuma wutar lantarki.

Kwamishinan ya ce kamfanin zai rika biyan gwamnati naira miliyan 50 a shekarar farko-farkon yarjejeniyar, a shekarun gaba Kuma ya rika biyan miliyan 100, haka zalika a shekarun karshen karshe na yarjejeniyar kamfanin zai rika biya naira miliyan 200 a duk wata.

kwamishinan muhalli
Getso ya kuma ce, kamfanin zai ɗauki ma’aikata sama da dubu hudu ciki har da injiniyoyi, kuma za su ninka albashin ma’aikatan da aka basu har sau uku.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...