An Dakatar da Sarkin Zurmi bisa zargin Haɗa Kai da Yan Bindiga

Date:

Daga khalifa Abdullahi Maikano

Gwamnatin jihar Zamfara ta dakatar da Mai Martaba Sarkin Zurmi a Jihar Zamfara, Alhaji Atiku Abubakar bisa zargin sa da hannu a karuwar hare-haren ‘yan bindiga a masarautarsa.


 Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa Mai dauke da sa hannun mukaddashin sakataren gwamnatin jihar Zamfara Alhaji Kabiru Balarabe Wadda kuma aka rabawa manema labarai a Gusau.


 Sanarwar ta ce, an kafa wani kwamiti na mutum 9 da zai binciki zargin a karkashin jagorancin tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Ibrahim Wakkala Muhammad da sauran manyan jami’an gwamnati ciki har da wakilan hukumomin tsaro.


 A cewar sanarwar, ana sa ran kwamitin zai gabatar da rahotonsa a cikin makonni 3.


 A halin yanzu, Alhaju Bello Suleiman (Bunun kanwa) shine zai kula da lamuran masarautar da gaggawa

91 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Maikwatashi: Tsohon kwamishinan Ilimi ya rubutawa gwamnan Kano budaddiyar Wasika

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Alhaji Muhammad Sanusi...

Gwamnatin Kano ta sauyawa makarantar mata ta Mai Kwatashi matsugunni

Ma'aikatar Ilimi ta Jihar Kano ta ɗauke Karantar Sakandare...

Sule Lamido, Ya Yi Barazanar Maka Shugabannin PDP a Kotu

  Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana...

Tsofaffin Kansiloli Sun Yi Saukar Alƙur’ani da Addu’a na Musamman ga Gwamna Abba

  Ƙungiyar tsofaffin kansiloli na jihar Kano ta gudanar da...