An Dakatar da Sarkin Zurmi bisa zargin Haɗa Kai da Yan Bindiga

Date:

Daga khalifa Abdullahi Maikano

Gwamnatin jihar Zamfara ta dakatar da Mai Martaba Sarkin Zurmi a Jihar Zamfara, Alhaji Atiku Abubakar bisa zargin sa da hannu a karuwar hare-haren ‘yan bindiga a masarautarsa.


 Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa Mai dauke da sa hannun mukaddashin sakataren gwamnatin jihar Zamfara Alhaji Kabiru Balarabe Wadda kuma aka rabawa manema labarai a Gusau.


 Sanarwar ta ce, an kafa wani kwamiti na mutum 9 da zai binciki zargin a karkashin jagorancin tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Ibrahim Wakkala Muhammad da sauran manyan jami’an gwamnati ciki har da wakilan hukumomin tsaro.


 A cewar sanarwar, ana sa ran kwamitin zai gabatar da rahotonsa a cikin makonni 3.


 A halin yanzu, Alhaju Bello Suleiman (Bunun kanwa) shine zai kula da lamuran masarautar da gaggawa

91 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Korar ma’aikata a Kano: Bashir Gentile ya yiwa Faizu Alfindiki martani mai zafi

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Masanin kimiyar siyasa kuma mai sharhi...

Sakataren kungiyar NRO Abdulkadir Gude ya rasu

Allah ya yi wa dattijo, kuma Sakataren kungiyar Northern...

Gwamnatin da ta ke korar Ma’aikata ba ta Cancanci Wa’adi na biyu ba – Faizu Alfindiki

Daga  Maryam Muhammad Ibrahim   Abin takaici ne ganin yadda gwamnatin...

Zaizayar kasa: Gwamna Abba gida-gida ya raba diyyar Naira Miliyan 600 A Kano

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...