An Dakatar da Sarkin Zurmi bisa zargin Haɗa Kai da Yan Bindiga

Date:

Daga khalifa Abdullahi Maikano

Gwamnatin jihar Zamfara ta dakatar da Mai Martaba Sarkin Zurmi a Jihar Zamfara, Alhaji Atiku Abubakar bisa zargin sa da hannu a karuwar hare-haren ‘yan bindiga a masarautarsa.


 Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa Mai dauke da sa hannun mukaddashin sakataren gwamnatin jihar Zamfara Alhaji Kabiru Balarabe Wadda kuma aka rabawa manema labarai a Gusau.


 Sanarwar ta ce, an kafa wani kwamiti na mutum 9 da zai binciki zargin a karkashin jagorancin tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Ibrahim Wakkala Muhammad da sauran manyan jami’an gwamnati ciki har da wakilan hukumomin tsaro.


 A cewar sanarwar, ana sa ran kwamitin zai gabatar da rahotonsa a cikin makonni 3.


 A halin yanzu, Alhaju Bello Suleiman (Bunun kanwa) shine zai kula da lamuran masarautar da gaggawa

91 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...