Faduwar Kwale-Kwale: An gano Gawar Mutane 97 a Kebbi – Atiku Bagudu

Date:

Gwamna Atiku Bagudu na Jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya ya ce an gano gawar mutum 97 jumilla na waɗanda jirgin ruwa ya kife da su a garin Warrah na Ƙaramar Hukumar Ngaski da ke jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a Birnin Kebbi lokacin da yake karɓar baƙuncin ‘yan Majalisar Wakilan Najeriya da suka je yi masa ta’aziyya game da hatsarin, kamar yadda kamfanin labarai na NAN ya ruwaito.

Sakataren Gwamnati Babale Umar-Yauri wanda ya wakilci gwamnan, ya ce an binne mutanen yayin da aka ceto mutum 22 da ransu.

Tun a ranar 2 ga watan Yuni jirgin ya kife da fasinjojin cikinsa bayan ya taso daga Minna a Jihar Neja ɗauke da ‘yan kasuwa da masu haƙar ma’adanai, inda ya halaka mutum kusan 100.

46 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...