Faduwar Kwale-Kwale: An gano Gawar Mutane 97 a Kebbi – Atiku Bagudu

Date:

Gwamna Atiku Bagudu na Jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya ya ce an gano gawar mutum 97 jumilla na waɗanda jirgin ruwa ya kife da su a garin Warrah na Ƙaramar Hukumar Ngaski da ke jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a Birnin Kebbi lokacin da yake karɓar baƙuncin ‘yan Majalisar Wakilan Najeriya da suka je yi masa ta’aziyya game da hatsarin, kamar yadda kamfanin labarai na NAN ya ruwaito.

Sakataren Gwamnati Babale Umar-Yauri wanda ya wakilci gwamnan, ya ce an binne mutanen yayin da aka ceto mutum 22 da ransu.

Tun a ranar 2 ga watan Yuni jirgin ya kife da fasinjojin cikinsa bayan ya taso daga Minna a Jihar Neja ɗauke da ‘yan kasuwa da masu haƙar ma’adanai, inda ya halaka mutum kusan 100.

46 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...