Faduwar Kwale-Kwale: An gano Gawar Mutane 97 a Kebbi – Atiku Bagudu

Date:

Gwamna Atiku Bagudu na Jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya ya ce an gano gawar mutum 97 jumilla na waɗanda jirgin ruwa ya kife da su a garin Warrah na Ƙaramar Hukumar Ngaski da ke jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a Birnin Kebbi lokacin da yake karɓar baƙuncin ‘yan Majalisar Wakilan Najeriya da suka je yi masa ta’aziyya game da hatsarin, kamar yadda kamfanin labarai na NAN ya ruwaito.

Sakataren Gwamnati Babale Umar-Yauri wanda ya wakilci gwamnan, ya ce an binne mutanen yayin da aka ceto mutum 22 da ransu.

Tun a ranar 2 ga watan Yuni jirgin ya kife da fasinjojin cikinsa bayan ya taso daga Minna a Jihar Neja ɗauke da ‘yan kasuwa da masu haƙar ma’adanai, inda ya halaka mutum kusan 100.

46 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...

Kananan Hukumomin Tarauni Rogo da Doguwa sun zamo koma baya wajen yin rijistar Masu zabe a Kano

Rahotanni sun nuna cewa ya zuwa yanzu kananan hukumomin...