Faduwar Kwale-Kwale: An gano Gawar Mutane 97 a Kebbi – Atiku Bagudu

Date:

Gwamna Atiku Bagudu na Jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya ya ce an gano gawar mutum 97 jumilla na waɗanda jirgin ruwa ya kife da su a garin Warrah na Ƙaramar Hukumar Ngaski da ke jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a Birnin Kebbi lokacin da yake karɓar baƙuncin ‘yan Majalisar Wakilan Najeriya da suka je yi masa ta’aziyya game da hatsarin, kamar yadda kamfanin labarai na NAN ya ruwaito.

Sakataren Gwamnati Babale Umar-Yauri wanda ya wakilci gwamnan, ya ce an binne mutanen yayin da aka ceto mutum 22 da ransu.

Tun a ranar 2 ga watan Yuni jirgin ya kife da fasinjojin cikinsa bayan ya taso daga Minna a Jihar Neja ɗauke da ‘yan kasuwa da masu haƙar ma’adanai, inda ya halaka mutum kusan 100.

46 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Na sauke nauyin da Tinubu ya ɗora min – Gwamnan riko na jihar Rivers

Vice-Admiral Ibok-Ete Ibas (Mai ritaya), wanda shi ne gwamnan...

Cin Gashin Kan Kananan Hukumomi: Kawu Sumaila ya jinjinawa Gwamnan Kano

Sanatan da ke wakiltar Kano ta Kudu a Majalisar...

Gwamna Yusuf Ya Shirya Baiwa Kananan Hukumomin Kano Cikakken ‘Yan cin Kai

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Majalisar Zartarwa ta jihar Kano ta Amince da kashe Naira Biliyan 18 don aiwatar da wasu aiyuka

  Majalisar zartarwar jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir...