Sojojin Najeriya sun ‘kashe’ ‘yan ISWAP guda 50

Date:

Mayaƙan ƙungiyar ISWAP fiye da 50 ne rundunar sojan Najeriya ta ce ta kashe a Jihar Borno ranar Laraba.

Mai magana da yawun rundunar, Birgediya Janar Yerima Mohammed, ya ce dakarunsu sun yi nasarar kashe ‘yan bindigar ne yayin da suka yi yunƙurin kai hari a Ƙaramar Hukumar Damboa da ke Borno.

Dakarun rundunar musamman ta Operation Hadin Kai ne suka samu nasarorin tare da taimakon sojojin sama, a cewarsa.

“‘Yan ta’addan sun kai hari garin da dukkan ƙarfinsu da manyan motoci masu ɗauke da bindigogi guda 12 da makaman harbo jirgi da babura da kuma ababen fashewa,” a cewarsa cikin wata sanarwa.

“Jajirtattun sojojin sun daƙile harin sannan suka lalata motoci masu silke tare da kashe ‘yan ta’addan ISWAP 50, abin da ya sa wasu suka tsere sakamakon luguden wuta daga sojojin sama.”

Da yake mayar da martani kan lamarin, Babban Hafsan Sojan Ƙasa Manjo Janar Faruk Yahaya ya taya dakarun murna game da nasarar da suka samu.

A wannan makon ne ƙungiyar ta sanar da naɗa Albarnawiy a matsayin shugabanta bayan ta yi iƙirarin kashe shugaban Boko Haram Abubakar Shekau.

98 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...