Sojojin Najeriya sun ‘kashe’ ‘yan ISWAP guda 50

Date:

Mayaƙan ƙungiyar ISWAP fiye da 50 ne rundunar sojan Najeriya ta ce ta kashe a Jihar Borno ranar Laraba.

Mai magana da yawun rundunar, Birgediya Janar Yerima Mohammed, ya ce dakarunsu sun yi nasarar kashe ‘yan bindigar ne yayin da suka yi yunƙurin kai hari a Ƙaramar Hukumar Damboa da ke Borno.

Dakarun rundunar musamman ta Operation Hadin Kai ne suka samu nasarorin tare da taimakon sojojin sama, a cewarsa.

“‘Yan ta’addan sun kai hari garin da dukkan ƙarfinsu da manyan motoci masu ɗauke da bindigogi guda 12 da makaman harbo jirgi da babura da kuma ababen fashewa,” a cewarsa cikin wata sanarwa.

“Jajirtattun sojojin sun daƙile harin sannan suka lalata motoci masu silke tare da kashe ‘yan ta’addan ISWAP 50, abin da ya sa wasu suka tsere sakamakon luguden wuta daga sojojin sama.”

Da yake mayar da martani kan lamarin, Babban Hafsan Sojan Ƙasa Manjo Janar Faruk Yahaya ya taya dakarun murna game da nasarar da suka samu.

A wannan makon ne ƙungiyar ta sanar da naɗa Albarnawiy a matsayin shugabanta bayan ta yi iƙirarin kashe shugaban Boko Haram Abubakar Shekau.

98 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...