Mun kafa APC akida a Kano don dawo da Martabar APC – Dan Bilki Kwamanda

Date:

Fitaccen dan jam’iyyar APC da ke jihar Kano a arewacin Najeriya Alhaji Abdulmajid Dan Bilki Kwamanda ya shaida wa BBC cewa sun kafa abin da suka kira ‘APC Akida’ ne domin dawo da martabar jam’iyyar a jihar ta Kano.

Dan Bilki Commander, wanda na hannun-daman shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ne da suka dade suna gwagwarmayar siyasa tare, ya kara da cewa gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ba ta kishin talakawa shi ya sa suka balle suka kafa ‘APC Akida’ domin wayar da kan jama’a kan irin illolin da take yi wa talakawa.

Ya kara da cewa nan gaba kadan za su fito da cikakkun bayanai kan yadda za su kwace ikon dukkan APC daga hannun magoya bayan gwamnatin jihar.

A cewarsa: “Gwamnatin jihar Kano ba ta kishin talakawa don haka muke ganin bai kamata mu ci gaba da tafiya tare da ita ba. mu ne muka kafa jam’iyyar APC kuma mun lura cewa ba sa bin ka’idoji da jam’iyyar ta shimfida shi ya sa muka balle daga cikinsu.”

Ya musanta zargin da ke cewa sun kafa APC Akida ne saboda korar da jam’iyyar ta APC ta yi musu, yana mai cewa “ai mu babu wanda ya isa ya kore mu daga wannan jam’iyyar domin da mu aka yanke mata cibiya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...