Sauyawa Nigeria Suna: Buhari ya Mayar da Martani

Date:

Gwamnatin Najeriya ta mayar da martani kan batun sauya wa ƙasar suna zuwa United African Republic (UAR) da yake ta jan hankalin ƴan ƙasar a yau.

Fadar shugaban Najeriya ta nesanta kanta daga wannan lamari, inda ta ce ba ita ta gabatar da ƙudurin sauya sunan ƙasar ba.

Mai taimaka wa shugaban ƙasar na musamman kan kafofin sada zumunta Bashir Ahmad ne ya wallafa a shafin Tuwita cewa Shugaba Buhari ba shi da hannu a batun sauya sunan.

“Ba gwamnatin Najeriya ko Shugaba Buhari ne suka miƙa buƙatar sauya sunan ba, mutane ne ƴan ƙasa suka yi hakan a wajen jin ra’ayoyin jama’a.

“Amma tuni wasu mutane suka ɗauki abin suka ɗora a ka suna zargin shugaban ƙsa wanda ba shi da hannu sam a ciki,” a cewar saƙon na Bashir.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...

Ra’ayi:‎Tsarin Kwankwasiyya ya dora Kano a gwadaben cigaba a mulkin Gwamna Abba Kabir -Adamu Shehu Bello

‎ ‎Ra’ayi ‎ ‎Daga Adamu Shehu Bello (Bayero Chedi), Jigo a Kwankwasiyya...