Sauyawa Nigeria Suna: Buhari ya Mayar da Martani

Date:

Gwamnatin Najeriya ta mayar da martani kan batun sauya wa ƙasar suna zuwa United African Republic (UAR) da yake ta jan hankalin ƴan ƙasar a yau.

Fadar shugaban Najeriya ta nesanta kanta daga wannan lamari, inda ta ce ba ita ta gabatar da ƙudurin sauya sunan ƙasar ba.

Mai taimaka wa shugaban ƙasar na musamman kan kafofin sada zumunta Bashir Ahmad ne ya wallafa a shafin Tuwita cewa Shugaba Buhari ba shi da hannu a batun sauya sunan.

“Ba gwamnatin Najeriya ko Shugaba Buhari ne suka miƙa buƙatar sauya sunan ba, mutane ne ƴan ƙasa suka yi hakan a wajen jin ra’ayoyin jama’a.

“Amma tuni wasu mutane suka ɗauki abin suka ɗora a ka suna zargin shugaban ƙsa wanda ba shi da hannu sam a ciki,” a cewar saƙon na Bashir.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Pyramid of Heart sun kai tallafin na’urar Oxygen Concentrated Asibitin Murtala dake Kano

Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhd dake Kano ya yabawa...

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...