Sauyawa Nigeria Suna: Buhari ya Mayar da Martani

Date:

Gwamnatin Najeriya ta mayar da martani kan batun sauya wa ƙasar suna zuwa United African Republic (UAR) da yake ta jan hankalin ƴan ƙasar a yau.

Fadar shugaban Najeriya ta nesanta kanta daga wannan lamari, inda ta ce ba ita ta gabatar da ƙudurin sauya sunan ƙasar ba.

Mai taimaka wa shugaban ƙasar na musamman kan kafofin sada zumunta Bashir Ahmad ne ya wallafa a shafin Tuwita cewa Shugaba Buhari ba shi da hannu a batun sauya sunan.

“Ba gwamnatin Najeriya ko Shugaba Buhari ne suka miƙa buƙatar sauya sunan ba, mutane ne ƴan ƙasa suka yi hakan a wajen jin ra’ayoyin jama’a.

“Amma tuni wasu mutane suka ɗauki abin suka ɗora a ka suna zargin shugaban ƙsa wanda ba shi da hannu sam a ciki,” a cewar saƙon na Bashir.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NAHCON ta sanar da ranar da za a fara jigilar Maniyatan Nigeria zuwa kasar Saudiyya

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar kula da aikin hajji ta...

Hisbah ta rushe wajen da aka ce sawun Ma’aiki ya fito a jihar Kano

    Hukumar Hisbah ta kai samame tare da rushe wani...

ƴan siyasa ne su ka kashe Arewacin Nigeria — Inji Gwamna Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa ‘yan...

Shugaban Karamar hukumar Bagwai ya kaddamar da aikn gada ta sama da Naira Miliyan 160

Daga Shu'aibu Sani Bagwai   Karamar hukumar Bagwai a jihar Kano...