Muqabala : Mai aljana yace Duk abin Daya fada Karya ne, Bai Auri aljana ba

Date:


Daga Umar Usman Sani Mainagge


Gwamnatin jihar Kano ta titsiye Mutuminan dan Kofar Na’isa da yayi da’awar ya auri aljanna har sun haifi ‘ya’ya da ita.


A gudanar da titsiyen ne a ofishin Kwamishinan ma’aikatar addini ta jihar Kano Dr. Tahar Baba Impossible dake gidan murtala a Nan birnin Kano.


 Tun a baya dai Ahmad Ali dake unguwar k/Na’isa Wanda akafi sani da Mai aljana yayi shuhurane da hulda da aljana da bada magungunan gargajiya, harma ya shaidawa kafafan yada labarai dana sada zumunta cewar wai ya auri aljana mai suna ummusibyan harma sun haifi ‘ya’ya tare.


Wancan furuci na Mai aljana ya baiwa Mutane mamaki sosai Saboda yadda yace mahaifin aljanar ne ya aura masa ita Saboda Dama shi a wajen aljanu ya girma sun Saba da juna sosoi.
To Bayan wancan furuci al’umma sun Yi ta kalubalantar Mai aljana ,hakan tasa gwamnatin Jihar Kano magantuwa Saboda yadda al’ummar suka Dauki Maganar da Kuma gujin kada Shi Mai aljanna ya jefa Mutane Cikin bata. Shi ne yasa Gwamnatin ta shirya Wannan Zama a Wannan Rana.


To sai dai a0 Mai aljana yayi karo da goshi jirgi domin yace ya janye duk kalamansa na baya tare da zubda makamansa bayan daya Sha matsa irinta Mai a gaban kwamashinan addinai.
 Bayan janye bayanan da yayi a baya Mai aljana ya shaidawa Duniya cewa ya saki Matarsa Amma aljanar har saki uku a gaban al’umma a ofishin kwamashinan Dr. Tahar Baba impossible.


Wakilin Kadaura24 ya tambayi Mai aljana cewa a Bayan mun ji matarka Mutum tace har raba Kwana suke da amaryarka aljana” Mai aljana sai ya kada Baki yace ” kawai dai ta Fadi hakan ne domin ta Kare Mana Abincin mu, Amma Karya take Yi.

 A Jawabinsa Kwamishinan harkokin addini na Kano Dr Tahir Baba Impossible yace sun shirya Titsiyen ne domin Gudun kada al’umma su fada Haka ta sanadiyyar kalaman Mai aljanar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...