Da dumi-dumi: Ba Gaggawar Kara kudin Man Fetir muke ba, Inji Buhari

Date:

Daga Surayya Abdullah Tukuntawa


 Gwamnatin Tarayya tace ba ta gaggawa don kara farashin man fetur ba, a cewar Timipre Sylva, Karamin Ministan Man Fetur
 Sylva ya bayyana hakan ne yayin da take mayar da martani ga shawarar kungiyar gwamnonin Najeriya (NGF) cewa tana bukatar farashin mai ya koma  N380 ko N408.5 ga kowane litre.
 A wani taro da suka gabatar, gwamnonin sun nemi a yi wa dokar kwastam ta kasa kwaskwarima tare da cire tallafin mai ba tare da bata lokaci ba, suna masu cewa tsarin tallafin da ake bayarwa a yanzu ba mai dorewa ba ne, kuma masu fasa-kwauri da ‘yan kasuwa da ke cinikin ta haramtacciyar hanya ne kawai ke cin gajiyar sa.
 Shawarwarin da gwamnonin suka bayar sun haifar da fushi da fusata al’ummar a duk fadin kasar nan kamar yadda yawancin ‘yan Najeriya suka ce zai kara wahala a kasar.


 Amma a nasa martanin, Sylva ya tabbatarwa da ‘yan Nijeriya cewa ba za a kara farashin mai a watan Yuni ba.


 “Ya zama dole a tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa duk da irin dimbin nauyin da ke tattare da tattalin arziki, Gwamnatin Tarayya ba t gaggawa take ba don ta kara farashin Man fetur don yin la’akari da gaskiyar kasuwar yanzu.”

 “Dangane da wannan, Ina so in yi kira ga masu sayar da kayayyakin man fetur da su guji shiga duk wasu ayyuka da ka iya kawo cikas ga tsarin samar da kayayyaki da rarraba su a yayin da nake kira ga jama’a da su guji karbar irin wancan rahoton saboda Kamfanin Man Fetur na Najeriya (  NNPC) yana da wadataccen man fetur don sayarwa al’ummar kasar nan Cikin Sauki

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...