Tahajjud: Yan Bindiga sun Sace Masallata 40 a Wani Masallaci dake Katsina

Date:

Akalla wasu bayin Allah Musulmi 40 ne ‘yan bindiga suka sace a yayin da suke gudanar da Sallah Tahajjud, wata sallar tsakar dare da ake gudanarwa a cikin watan Ramadan, a wani masallaci da ke garin Jibiya na jihar Katsina.


 Mazauna garin sun ce ‘yan bindiga da dama sun kai hari a masallacin da misalin karfe 2 na daren Litinin kuma suka tafi da masu ibadar.


 Rahotannin sun nuna cewa masu garkuwan da farko sun Debi masallata 47, ciki harda mata da yara, amma daga baya bakwai suka dawo.
 “Ya zuwa yanzu mun tabbatar mutane 40 ne suka bata yayin harin,” in ji wani mazaunin garin da ya bukaci a sakaya sunansa.


 Wani mazaunin garin Mai Suna Lawal Jibiya, ya ce mazauna kauyukan da suke kusa dasu sun sanar da su game da harin, bayan sun ga hucewar ‘yan bindigar da ke kan hanyar zuwa garin.


 Ya ce daruruwan matasa da ‘yan banga da ke cikin garin sun Yi shirin ko ta kwana don tunkarar’ yan ta’addan, amma maharan sai suka sauya hanyarsu ta shiga Garin suka shiga garin ta mashigar yamma.


 “Mun tsammacesu daga mashigar gabas ta hanyar Daddara, Kukar Babangida ko Magama amma sai suka wuce bayan gari suka yada zango a Jibawa.


 “Daga Jibawa daga nan suka zagaya zuwa mashigar yamma kusa da asibitin Yunusa Dantauri kuma suka farma wani masallaci a bayan gari,” in ji shaidar.


 A cewarsa, ‘yan fashin ba su yi harbi ba  har sai da suka gama aikin .


 Jibiya, wani gari ne da ke kan iyaka tsakanin Najeriya da Nijar, na daya daga cikin wuraren da ake yawan yin garkuwa da Mutane da kuma ayyukan ‘yan fashi.

89 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...