Sojoji sun Kama Mutane 10 da ake zargin Yan Boko Haram ne a Kano

Date:

Sojojin Najeriya sun kai wani samame wani masallaci da ke Filin Lazio unguwar Hotoro cikin birnin Kano kuma sun kama kimanin mutane 10 da ake zargin ‘yan Boko Haram ne a yammacin Asabar din data gabata.


 Shaidun gani da ido sun shaidawa Solacebase cewa aikin wanda bai wuce awa daya ba ya gudana yayin da al’ummar musulmin yankibke gudanar da buda baki.


 Lamarin ya haifar da firgici da tsoro ga mazauna yankin, yayin da Sojoji Kuma suka gudanar da bincike a wasu gidaje .


 Solacebase ta rawaito cewa nan da nan bayan aikin, Wasu Daga Cikin al’ummar yankin suka kauracewa unguwar Saboda tunanin sojojin zasu iya komawa unguwar.

 Lokacin da Majiyar Kadaura24 ta tuntube  kakakin rundunar a nanKano Kyaftin Irabor ya yi alkawarin idan ya kammala tattara bayanan Zai sanar da Manema labarai a Ranar Lahadi nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Pyramid of Heart sun kai tallafin na’urar Oxygen Concentrated Asibitin Murtala dake Kano

Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhd dake Kano ya yabawa...

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...