Sojoji sun Kama Mutane 10 da ake zargin Yan Boko Haram ne a Kano

Date:

Sojojin Najeriya sun kai wani samame wani masallaci da ke Filin Lazio unguwar Hotoro cikin birnin Kano kuma sun kama kimanin mutane 10 da ake zargin ‘yan Boko Haram ne a yammacin Asabar din data gabata.


 Shaidun gani da ido sun shaidawa Solacebase cewa aikin wanda bai wuce awa daya ba ya gudana yayin da al’ummar musulmin yankibke gudanar da buda baki.


 Lamarin ya haifar da firgici da tsoro ga mazauna yankin, yayin da Sojoji Kuma suka gudanar da bincike a wasu gidaje .


 Solacebase ta rawaito cewa nan da nan bayan aikin, Wasu Daga Cikin al’ummar yankin suka kauracewa unguwar Saboda tunanin sojojin zasu iya komawa unguwar.

 Lokacin da Majiyar Kadaura24 ta tuntube  kakakin rundunar a nanKano Kyaftin Irabor ya yi alkawarin idan ya kammala tattara bayanan Zai sanar da Manema labarai a Ranar Lahadi nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...