Sojoji sun Kama Mutane 10 da ake zargin Yan Boko Haram ne a Kano

Date:

Sojojin Najeriya sun kai wani samame wani masallaci da ke Filin Lazio unguwar Hotoro cikin birnin Kano kuma sun kama kimanin mutane 10 da ake zargin ‘yan Boko Haram ne a yammacin Asabar din data gabata.


 Shaidun gani da ido sun shaidawa Solacebase cewa aikin wanda bai wuce awa daya ba ya gudana yayin da al’ummar musulmin yankibke gudanar da buda baki.


 Lamarin ya haifar da firgici da tsoro ga mazauna yankin, yayin da Sojoji Kuma suka gudanar da bincike a wasu gidaje .


 Solacebase ta rawaito cewa nan da nan bayan aikin, Wasu Daga Cikin al’ummar yankin suka kauracewa unguwar Saboda tunanin sojojin zasu iya komawa unguwar.

 Lokacin da Majiyar Kadaura24 ta tuntube  kakakin rundunar a nanKano Kyaftin Irabor ya yi alkawarin idan ya kammala tattara bayanan Zai sanar da Manema labarai a Ranar Lahadi nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...