Wasu Yara biyu sun Rasa Rayukansu a wani kududdufi a Mariri

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

Wasu Mutane biyu, Umar Auwalu mai shekaru 15 da Muhammed Nafis, 20, a ranar Juma’a sun Rasa Rayukansu a cikin wani kududdufi a Mariri Ramin Kalanzir da ke karamar Hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Alhaji Saminu Abdullahi, jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a a Kano.

Abdullahi ya ce hukumar kashe gobara ta samu kiran gaggawa da misalin karfe 07:57 na safe daga wani mai suna Mustapha Musa inda nan take ta aika da jami’an ta zuwa inda lamarin ya faru da misalin karfe 08:10 na safe.

“An fitar da su daga cikin kududdufin kuma daga baya an mika gawarwakinsu ga Dagacin unguwar Sheka Gabas, Alhaji Umar Yunusa,” in ji Abdullahi.

Jami’in Hulda da jama’a na hukumar kashe gobarar ya ce har yanzu ba a gano musabbabin mutuwar su ba, amma ana ci gaba da bincike.

Ya shawarci iyayen yara da kuma masu unguwanni dsu Rika kula da zirga-zirgar ya’yansu a musamman ga wadanda suke kusa da kududdufi don hana faruwar abubuwa irin wadannan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...