Al’ummar Unguwar Yamadawa a Kano sun kama Yan Bindiga 2

Date:

Abdulrashid B Imam

Mazauna Unguwar Yamadawa, Ɗorayi Babba da ke karamar Hukumar Gwale a Jihar Kano sun kame wasu da ake zargin ’yan fashi da makami ne yayin da suke kokarin yi wa wani mutum fashi a yankin da misalin karfe 11.00 na daren Laraba.
 Wani ganau ya ce lamarin ya faru ne a daren Laraba bayan da wadanda ake zargin su biyu suka fito da bindiga a kokarin yi wa wani mutum fashi a yayin da suka tuka mota zuwa gidansa.

 Sun ce lamarin ya ja hankalin mutanen da ke kusa kuma nan da nan suka fada kan ‘yan bindigar wadanda suka bude wuta kuma suka yi yunkurin tserewa da keken mai kafa uku.
 Sai dai kuma mutanen sun yi fito-na-fito da ‘yan bindigan, sun kame su tare da mika su ga‘ yan sanda da ke yankin.


 A cewar daya daga cikin shaidun, ‘yan sanda sun tafi da wadanda ake zargin zuwa asibiti saboda mummunar azabtar da su da mazauna yankin suka yi musu.


 Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da cafke wadanda ake zargin‘ yan fashin ne a ranar Alhamis.


 Ya ce an samu bindiga da wuka daga wanda ake zargin a yayin da suke kokarin kwace wata mota kirar Toyota Corolla

351 COMMENTS

  1. 07:40. Болельщики считают, что Усик побьёт Джошуа. Комментирует Эдди Хирн. 25.08.21. 19:10. Энтони Джошуа сравнил себя с Месси и рассказал о подготовке к Усику. 24.08.21. 13:05. Энтони Джошуа назвал ключ к Джошуа Усик смотреть онлайн Усик против Джошуа – Костя Цзю

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...