Yanzu-Yanzu : An dakatar da Hadiza Bala Usman a Matsayin MD ta NPA

Date:

An dakatar da Hadiza Bala Usman a matsayin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Najeriya (NPA).


 An fara nada ta ne a 2016 bayan korar Habib Abdullahi wanda Shugaba Muhammadu Buhari ya dakatar da wa’adinsa na biyu.


 Babu wani dalili da aka bayar na dakatar da Hadiza Bala Usman wanda aka sake nada ta a karo na biyu a watan Janairu.


 Wata majiya a Ma’aikatar Sufuri, wacce ke kula da NPA, ta yi ishara da cewa Akwai takun saka tsakanin Ministan, Chibuike Rotimi Amaechi, da Usman a ‘yan kwanakin nan.


 Majiyar, wacce kuma mataimaki ce ga Ministan, ta ce Amaechi ya damu matuka da halin wuce gona da iri na Hadiza Usman.


 “Ee, an dakatar da MD a safiyar ranar Alhamis amma Ministan zai bayar da cikakken bayani a ranar Juma’a.


 “Ministan da wasu mambobin ma’aikatar suna Jos a halin yanzu don wani shiri kuma an shirya zai yi wa manema labarai bayani game da batun.
 “Ba a ba da dalilin dakatar da ita ba amma ina iya tabbatar muku da cewa an dakatar da ita,” in ji shi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...