Sallah :Ku yiwa al’umma Sauki Saboda halin da ake ciki – Shugaban Kantin kwari ga Yan Kasuwar

Date:

Daga Rabi’u Usman

Anyi Kira ga yan Kasuwa Musamman Kasuwar Kantin Kwari dasu Kasance Masu yiwa Jama’a Sauki Dai-dai Lokacin da ake Cikin Hada Hadar Siyayyar Kayan Sallah a Wannan lokaci na Karatowar Bikin Sallah Karama.

Shugaban Hadaddiyar Kungiyar ‘yan Kasuwar Kantin Kwari Alhaji Sharu Kabiru ne yayi Kiran a ta Bakin Mai Magana da yawun Kungiyar Mansur Dan Dago Jim Kadan Bayan Fitowar Su Daga Gidan Mai Martaba Sarkin Kano Alh Aminu Ado Bayero da Mai Martaba Sarkin Bichi Alh Nasiru Ado Bayero yayin Ta’aziyyar Mahaifıyar Su Hajiya Maryam Mai Babban Daki.

Yana Mai Cewar, a Shekarar da ta Gabata Basu Samu Damar Gudanar da Kasuwancin Su ba Sakamakon Annobar Cutar Corona Virus data Addabi Duniya Baki Daya Sai a Wannan lokaci, yace ta Haka ne Zasu Saukakawa Jama’a Musamman a Wannan Lokacin da ake Cikin Watan Azumin Ramadana Mai Albarka.

Ya Kara da cewa, Sunyi Kira ga Kafatanin Masu Kamfanoni dasu Kasance Masu Saukakawa Jama’a Musamman yan Kasuwannin da Suke Siyayyar Kaya a Wajen Su (Diloli) a Sassan Jihohin Kasar Nan.

A Karshe dai Dan Dago yayi Kira ga Al’umma dasu Gujewa Fadawa Hurumin da ba Nasu ba, Musamman Masu Dogon Hannu a Kasuwanni da Suji tsoron Allah Su daina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...