Muna goyon bayan Rundunar yan sandan jihar Kano domin Inganta Tsaro a kano- Shugaban Masu sayar da filaye

Date:

Daga Rabi’u Usman

Biyo Bayan Kaddamar da Littafin da Rundunar Yan Sandan Jihar Kano ta yi, Wanda Za’a Dinga Wallafa Bayanan Dukkannin Masu Karbar Hayar Gidaje Ko kango da Filaye keyi a lungu da Sako a Fadin Jihar Kano Dama Kasa Baki Daya, Shugaban Kungiyar Masu Hada Hadar Filaye da Gidaje da Mamallaka Gidajen Haya na Kasa Alhaji Musa Khalil Hotoro ya Goyi Bayan Wannan Kudirin na Jami’an Yan Sanda Domin Samar da Ingantaccen tsaro a Jihar Nan dama Kas Baki Daya.

Yana Mai Jan Kunne da Gargadin Mambobin Kungiyar Su dasu Kasance Masu Baiwa Jami’an Yan Sanda Cikakken Hadin Kai Wajen Samar da tsaro a Duk inda Suke Domin tsarkake Harkokin Dillancin Su.

Musa Khalil ya lashi Takobin Gurfanar da duk Wanda Suka Kama Dan Kungiya da Karya Dokar Gwamnati da Kuma ta Jami’an tsaro a Gaban Shari’ah.

A Karshe yayi Kira ga Al’umma dasu Kasance Masu Taimakawa Jami’an Rundunar Yan Sandan Jihar Kano Wajen Bayar da Bayanan Sirri da Zarar Sunga Motsin Abin da Basu Amince da Shi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...