Muna goyon bayan Rundunar yan sandan jihar Kano domin Inganta Tsaro a kano- Shugaban Masu sayar da filaye

Date:

Daga Rabi’u Usman

Biyo Bayan Kaddamar da Littafin da Rundunar Yan Sandan Jihar Kano ta yi, Wanda Za’a Dinga Wallafa Bayanan Dukkannin Masu Karbar Hayar Gidaje Ko kango da Filaye keyi a lungu da Sako a Fadin Jihar Kano Dama Kasa Baki Daya, Shugaban Kungiyar Masu Hada Hadar Filaye da Gidaje da Mamallaka Gidajen Haya na Kasa Alhaji Musa Khalil Hotoro ya Goyi Bayan Wannan Kudirin na Jami’an Yan Sanda Domin Samar da Ingantaccen tsaro a Jihar Nan dama Kas Baki Daya.

Yana Mai Jan Kunne da Gargadin Mambobin Kungiyar Su dasu Kasance Masu Baiwa Jami’an Yan Sanda Cikakken Hadin Kai Wajen Samar da tsaro a Duk inda Suke Domin tsarkake Harkokin Dillancin Su.

Musa Khalil ya lashi Takobin Gurfanar da duk Wanda Suka Kama Dan Kungiya da Karya Dokar Gwamnati da Kuma ta Jami’an tsaro a Gaban Shari’ah.

A Karshe yayi Kira ga Al’umma dasu Kasance Masu Taimakawa Jami’an Rundunar Yan Sandan Jihar Kano Wajen Bayar da Bayanan Sirri da Zarar Sunga Motsin Abin da Basu Amince da Shi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...