Kano tayi datti, muna bukatar hanzari wajen magance matsalar sharar -Gwamna Ganduje

Date:


Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa

 Gwamnan jihar Kano Umar Abdullahi Ganduje ya yi tir da yanayin kazantar da jihar ke ciki a yunkurin gwamnatinsa na Kara daga darajar jihar Kano zuwa babban birnin a Duniya. 


 Gwamnan ya bayyana yayain taron Majalisar Zartarwa ta Wannan makon , inda yayin Zaman Majalisar wani kamfani ya ganatar d Kudirinsu na hada hannu da gwamnatin Jihar domin magance matsalar shara a Kano.


Ganduje yace hakan yanayin rashin kula da shara, kalubalen da yake haifarwa da kuma bukatar samar da mafita mai dorewa don ci gaban birnin na Kano.


Gwamna Ganduje ya ce jihar na ta yin shawarwari kan shirin cutar da jihar Kano gaba domin birnin yayi gogayya da sauran birane, amma kalubalen kula da shara yana kawo cikas ga burin hakan.


 Ya ce illar rashin kyakkyawan kulawa da shara ya mamaye ko’ina a Kano, wanda ke haifar da mummunan yanayi na lafiya kamar su cutar kansa da ire-iren matsalolin kiwon lafiya, lamarin da ke jawo wa gwamnati makudan kudade.


Gwamna Ganduje yace gwamnatin zata hada hannu da kamfanoni Masu Zaman kansu domin Kawo Karshen matsalar shara ta Hanyoyi daban-daban don cigaban Kano

113 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...