Ganduje ya yiwa Sarakunan Kano da Bichi ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsu

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana rasuwar Hajiya Maryam, Mai Babban Dakin Kano kuma matar marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero a matsayin babban Rashi ba ga al’ummar Jihar Kano ba kadai har da Kasa baki daya.

Ya nuna juyayinsa a madadin gwamnati da jama’ar jihar Kano ga Sarakunan Kano da Bichi, Alhaji Aminu Ado Bayero da Alhaji Nasiru Ado Bayero Daya bayan daya.

A cikin sakon ta’aziyya da kwamishinan yada labarai, Malam Muhammad Garba ya fitar, gwamnan, wanda ya kara bayyana marigayiyar a matsayin uwa mai ladabi da gaskiya mai tarbiyantar da yayanta kan tafarkin Allah, ya yi wa sarakuna ta’aziyyar Rasuwar mahaifiyarsu.

Ganduje ya ce mutuwar ta a wannan lokacin ta haifar da wani yanayi mai wahalar cikewa musamman ga ‘ya’yan ta maza guda biyu wadanda ke matukar bukatar jagora da shawarwari daga uwa.

Gwamnan ya roki Allah Madaukakin Sarki da ya sanya marigayir a Aljannah Firdausi da kuma karfin gwiwa ga dangin, da daukacin mutanen da ke Masarautar guda biyu don jure wannan babban rashi.

80 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...

Kananan Hukumomin Tarauni Rogo da Doguwa sun zamo koma baya wajen yin rijistar Masu zabe a Kano

Rahotanni sun nuna cewa ya zuwa yanzu kananan hukumomin...